Yau Laraba Majalisar Dattawan Najeriya za ta tantance ministoci bakwai

Bam ya tashi a wurare da dama a Ethiopia

‘Yansanda a Ethiopia sun ce an samu tashin bam a wurare hudu a birnin Bahir Dar na arewacin kasar.

Babu dai wani bayani kan ko an samu hasarar rayukka ko jikkata.

Wani kakakin ‘yansandan ya ce an kama mutane shida da ake tuhuma.

Zaman tankiya ya karu a yankin Amhara a baya-bayan nan, bayan wani samame da hukumomin suka kai kan kungiyoyin mayaka inda aka kama dubban mutane.

An yi ta zanga-zangar kin-jinin-gwamnati a wannan watan sakamakon kashe ‘yan kabilar Amhara fiye da 200 a yakin Oromia mai makwabtaka.

Masu aiko da rahotanni sun ce tashin bama-baman wata alama ce ta karuwar zaman dar-dar a Ethiopia wadda ke fama da tashe-tashe hankula iri daban-daban.

Leave a comment

Design a site like this with WordPress.com
Get started