
Shugaban Majalisar Dattawan Ahmad Lawan ne ya sanar da batun tantancewar a jiya Talata inda ya ce za a shafe zaman majalisar da za a yi yau domin tantance ministocin.
Cikin waɗanda za a tantance akwai Ibrahim El-Yakub daga Jihar Kano, Umana Okon Umana (Akwa Ibom), Henry Ikechukwu Iko (Abia), Ademola Adegoroye (Ondo), Odum Odi (Rivers).
Sauran su ne Goodluck Nnana Opia (Imo) da kuma Joseph Ukama (Ebonyi ).
A kwanakin baya ne dai wasu daga cikin ministocin Najeriya suka yi murabus saboda takarar da suka tsaya, lamarin da ya tilasta musu dole su yi murabus sakamakon sabuwar dokar zaɓe da ta tanadin haka.
Bam ya tashi a wurare da dama a Ethiopia
‘Yansanda a Ethiopia sun ce an samu tashin bam a wurare hudu a birnin Bahir Dar na arewacin kasar.
Babu dai wani bayani kan ko an samu hasarar rayukka ko jikkata.
Wani kakakin ‘yansandan ya ce an kama mutane shida da ake tuhuma.
Zaman tankiya ya karu a yankin Amhara a baya-bayan nan, bayan wani samame da hukumomin suka kai kan kungiyoyin mayaka inda aka kama dubban mutane.
An yi ta zanga-zangar kin-jinin-gwamnati a wannan watan sakamakon kashe ‘yan kabilar Amhara fiye da 200 a yakin Oromia mai makwabtaka.
Masu aiko da rahotanni sun ce tashin bama-baman wata alama ce ta karuwar zaman dar-dar a Ethiopia wadda ke fama da tashe-tashe hankula iri daban-daban.

Leave a comment